A cewar rahoton sashen fassara na Ofishin Yada Labaran Hauza, wadannan jam'iyyun na Lebanon sun fitar da sanarwa kamar haka:
Yanzu ma gwamnatin Amurka ta bayyana fuskarta ta ta'addanci da mummuna ta hanyar kai hari na laifuka kan kasar Venezuela wadda kawa ce. Sun bayyana harin a matsayin girman kai wanda ya saba wa dukkan dokoki da ka'idoji na kasa da kasa, da dabi'u na mutuntaka.
Taron jam'iyyun ya bayyana cewa wannan kutse yana nuna tunani na nuna fifiko da girman kai wanda gwamnatocin Amurka ke amfani da shi wajen mu’amala da sauran kasashen duniya. Sun kara da cewa wannan dabi’a ta fi tsanani a karkashin shugabancin wawa Donald Trump.
Jam'iyyun na Lebanon sun kara da cewa wannan mataki na Amurka babbar barazana ce ga zaman lafiya da tsaro na duniya, kuma keta hurumin kasa ne wacce take mamba a Majalisar Dinkin Duniya. Sanarwar ta yi nuni da cewa sace shugaba Nicolas Maduro da matarsa wani mummunan misali ne na fashin teku (piracy) a matakin kasa da kasa wanda ke da hatsari sosai.
Your Comment