Kafara yada labari ta Hauzah ta labarta cewa Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, Shaikh Ibrahim Zakzaky, kwanan nan ya wallafa wani rubutu a shafinsa na Instagram, inda ya yi nuni da muhimmancin Salatin Ibrahimi, yana tambaya da bayanin ma’anar Iyalan Annabi Muhammadu da Iyalan Annabi Ibrahim (A.S.). Ya ce: “Wasu mutane suna kuskuren ɗaukar cewa ‘iyalan Ibrahim’ suna nufin dukkan zuriyarsa baki ɗaya, har su haɗa da Sihyoniyawa, alhali kuwa Al‑Kur’ani ya bayyana cewa: ‘Azzalumai ba za su samu alkawari na ba.’”
Shaikh Zakzaky ya ƙara jaddada cewa zuriyar Annabi Ibrahim (A.S.) da ake nufi ita ce Annabawan da suka fito daga zuriyarsa, kuma wannan ne ma’anar Iyalan Annabi Ibrahim (A.S.) waɗanda ake girmamawa a Musulunci.
A ƙarshen bayaninsa, ya ce Iyalan Annabi Muhammadu (S.A.W.) sun haɗa da Imamai Ma’asumai (wadanda suka tsarkak daga kuskure), waɗanda suka haɗa da Ali, Fatima, Hassan, da Hussein (A.S.), da kuma wasu Imamai tara daga zuriyar Imam Hussein (A.S.), wanda gaba ɗaya suka zama Imamai goma sha biyu.
Your Comment