Rahoton Ofishin Yada Labaran Hauza, yana kawo muku jerin darussan sanin Imam Mahdi (A.S) mai taken “Zuwa Ga Al’umma Mai Manufa”, da nufin yaɗa koyarwa da ma’arifa dangane da Imamin Zamaninmu (Allah ya gaggauta bayyanarsa).
Daga cikin muhimman siffofin Imami da sharuɗɗan shugabanci akwai “Jagorancin Al’umma da Kawatuwa da Kyawawan Halaye”.
Jagorancin Al’umma na Imami
Tun da yake ɗan adam halitta ne da ke rayuwa a cikin jama’a, kuma al’umma tana da tasiri sosai a kan ruhinsa da halayensa, ya zama dole a samar da yanayi mai kyau na zaman takewa domin samun tarbiyya ta gari da kusanci ga Allah. Wannan kuma ba zai taɓa samuwa ba sai a ƙarƙashin inuwar kafa gwamnatin Ubangiji. Saboda haka, dole ne Imami kuma shugaban mutane ya kasance mai ikon tafiyar da al’amuran al’umma, ta hanyar amfani da koyarwar Alkur’ani da Sunnar Manzo (S) da kuma amfani da ƙwararrun mutane domin kafa tsarin gwamnatin Musulunci.
Kawatuwar Imami da Kyawawan Halaye
Imami wanda shi ne jagoran al’umma dole ne ya nisanci dukkan munanan ayyuka da dabi’un banza, a maimakon haka, ya mallaki dukkan kamalar ɗabi’u a matsayi mafi girma. Wannan kuwa domin shi ne mafi kyawun abin koyi ga mutane.
Imam Ridha (A.S) ya bayyana hakan inda yake cewa:
“Imami yana da wasu alamomi: Shi ne mafi ilimin mutane, mafi hikima, mafi takawa, mafi haƙuri, mafi jarumta, mafi kyauta, sannan kuma mafi yawan bauta a cikin mutane.” (Al-Khisal, juzu’i na 2, shafi na 527).
Bugu da ƙari, Imami a matsayinsa na magajin Manzo (S), burinsa shi ne ilimantarwa da tarbiyyantar da ɗan adam. Saboda haka, ya kamata shi kansa ya kasance ya rigaya ya kawatu da ɗabi’un Ubangiji fiye da kowa.
Imam Ali (A.S) ya faɗa a cikin wannan ma’ana:
“Duk wanda ya sanya kansa a matsayin shugaban mutane, to ya fara da ilimantar da kansa kafin ya ilimantar da wasu; sannan tarbiyyarsa (ga wasu) ta kasance ta hanyar ayyukansa kafin ta kasance ta hanyar harshensa.” (Nahjul Balagha, Hikima ta 73).
Wannan darasi zai ci gaba...
An ciro ne daga littafin “Negin-e Afarinesh”, tare da ɗan sauyi kadan
Your Comment