Friday 13 February 2026 - 21:29
Karance-karancen Muhawara | Kai Ne Ka Halitta? To, Kidaya Kuma Ka Canza Su!

Hauza/ Wani mutum da ya yi ikirarin cewa shi ne ya halicci wasu halittu, ya kasa bayar da amsoshi ga takamaiman tambayoyi game da halittar tasa, wanda hakan ya sa ya fadi a muhawarar kuma karyarsa ta bayyana.

A cewar Ofishin Yada Labaran Hauza, littafin "Muhawarwari 101 Masu Sha'awa" na Muhammad Muhammadi Eshtehardi ya tattara muhawarori daban-daban kan al'amuran akida da addini, wadanda za a rika wallafa su a hankali.

A zamanin Imam Sadik (A.S), wani mutum mai suna Ja'adu bin Dirham ya fara fito da wasu bidi'o'i da adawa da Musulunci, har ma ya samu wasu mabiya.

Wata rana, ya zuba laka da ruwa a cikin wata kwalba. Bayan wasu kwanaki, sai wasu kananan kwari da tsutsotsi suka bayyana a cikin wannan kwalbar. Ya fito gaban mutane ya yi ikirarin cewa: "Wadannan kwari da tsutsotsi ni ne na halitta su, domin ni ne silar bayyanarsu, don haka ni ne mahalicci kuma allansu."

Wasu gungun musulmi suka kai labarin nan ga Imam Sadik (A.S). Imam ya ce musu: "Ku gaya masa ya fadi nawa ne adadin wadannan kwari da ke cikin kwalabar? Nawa ne maza, nawa ne mata? Menene nauyinsu? Kuma ku nema a wurinsa ya canza siffarsu zuwa wata siffar daban, domin wanda ya halicci abu yana da ikon canza siffarsa."

Wannan rukunin mutane suka je suka gabatar da wadannan tambayoyi ga wannan mutumi da yake riya kansa a matsayin Allah. Ya kasa bayar da amsar ko daya daga cikin wadannan tambayoyi. Ta haka, shirinsa ya rushe, dabararsa kuma ta tonu a matsayin yaudara.

Madogara: Safinatul Bihar, Juzu'i na 1, Shafi na 157

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha