A cewar rahoton sashin fassara na Ofishin Yada Labaran Hauza, Hujjatul Islam Sayyid Abulqasem Razavi, Shugaban Majalisar Malaman Shi'a ta Ostiraliya kuma Limamin Juma'a na Melbourne, a cikin jawabinsa da ya yaba da matsayi da hali na Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci, ya jaddada cewa shi ba kawai shugaban al'ummar Iran ba ne, a'a, shi ne shugaban da ya dace ga al'ummar Musulunci, da fata na hakika na raunanan duniya, kuma mai kare hakkin wadanda aka zalunta a ko'ina.
Ya ci gaba da cewa, yana mai nuni ga matsayin babban jagoran juyin juya hali na musulunci wanda babu kwatankwacinsa: "Ina rokon Allah Ya kiyaye babban shugaban nan a karkashin kariya da goyon bayansa. Shi kamar zaki mai jaruntaka ne, ba ya tsoron fashewa da barazana, saboda haka barazanar maƙiyan ba za su iya sa shi firgita ko karkata ba."
Shugaban Majalisar Malaman Shi'a ta Ostiraliya ya kara da cewa: "Maƙiya da azzalumai sun manta da gaskiyar cewa, zaki idan ya ji rauni, ya fi hadari da ƙarfi. Tsattsarkan jinin tsantsar shuhada ba kawai bai raunana al'ummar Iran ba, sai dai ma ya kara musu ƙarfi, da juriya da azama."
Ya ci gaba da cewa, shugabancin Ayatullah Ali Khamenei a wannan zamanin shi ne kwatankwacin zahirin jaruntaka, juriya, nasara da taimakon Allah.
Wannan babban malamin addini, ya ci gaba da sukar ayyukan kafofin watsa labarai na ƙasashen waje, ya ce: "A Iran, filayen jiragen sama, layukan jiragen sama, sabis na dogo, tashoshin jiragen ƙasa, kantuna, gidajen cin abinci, da kasuwanni duk suna aiki bisa al'ada da kuzari. Abin takaici ne idan idanun kafofin watsa labarai sun kasance a rufe ga waɗannan gaskiyoyi. Da sun yi ƙoƙarin tafiya Iran, da sun ga gaskiya da idonsu, su ji da kunnuwansu."
Hujjatul Islam Sayyid Abulqasem Razavi a ƙarshe, ya jaddada cewa: "Yanzu lokaci ya yi da kafofin watsa labarai zasu dawo da darajar sana'arsu, domin yaduwar lalata a duniya, babban sakamakon aikin lalatattun kafofin watsa labarai ne masu cike da rashin aminci."
Your Comment